Sunday, October 6, 2019

ZINA BASHI CE
Mutumin yana cewa:
A lokacin da ina saurayina nasami Admission a Jami'a, bayan nafara karatun ne sai na hadu da wata Budurwa (Girlfriend) a cikin Jami'ar tamu muka 'kulla soyayya da ita tamkar ma'aurata, hardai tasami juna biyu, (yayi mata ciki kenan).
Da iyayenta suka gane sai suka tambaye ta wanda yayi mata ciki sai tace nine nayi mata.
Sai yayanta yataho nema na a fusace yana nufin
d'aukar mataki a kaina, yana zuwa saiya tambayeni kaine kayima qanwata ciki ko ???
Sai na amsa masa da cewa:
Wace ce, ni banma taba ganinta ba a rayuwata, ban santah ba. Sakamakon rashin hujjar da zasu kamani da ita dole suka 'kyaleni.
Bayan tsawon zamani, wata rana nadawo gida saina tarar da Mahaifiyata a dur'kushe tana tana kuka. Saina dur Qusa na daga ta sai tasake yanke jiki tafad'i 'kasa har sau uku saina tambaye ta a karo na qarshe:
"Ya Ummi Man ladzhi haddath (me ya faru mama)?
Sai tace: Qanwarkace gata can wani yayi mata ciki! Yace sai naji kamar an sokeni da mashi, hankali na ya tashi na tasa 'keyarta muka tafi wurin wanda tace yai mata cikin.
Da mukaje sai yafada min maganar data tayarmin da hankali.
Bawata magana bace face wadda na fadama yayan yarinyar da nayi
ma ciki a baya.(Ban santa ba, banma taba ganinta ba)!
Bayan zamani yaqara yin nisa sai nayi nufin yin aure nafara neman aure nasamu matar da nake so kuma a kasa lokaci akayi biki, ranar farko dana tare da ita saina sameta ba a matsayin budurwa ba.
Ma'ana tariga tayi zina, tuni hankalina ya tashi. Sai ta fadamin wata magana mai shiga rai.
"Don Allah karufa min asiri, ka suturta al'amarina kaima Allah sai ya suturta al'amarinka."
Yace sai nace a cikin zuciyata: Ya Rabby yakfy, yakfy. (Ma-ana Ya Mahalliccina ya isa haka ya isa haka).
Ya cigaba da cewa: Bayan mun kwashe shekaru da matata sai muka
haifi 'ya mace kyakkyawa gata da haske kamar wata. A lokacin da ta cika shekaru 6 a duniya sai gata wata rana ta shigo gida tana kuka. Me yafaru?
Ai me gadine yayi mata fyad'e! INNA LILLAHI WA INNA ILAIHI RAJI'UN
Aljazaa'u min jinsil amal! Wallahi duk tsiyar da kake sheqewa idan Allah
ta'ala yaga dama sai ya hada maka zafi kan zafi irin wannan! Yanzu kunga shi ya lalata 'yar mutane guda daya tak shi kuma an lalata masa guda uku! Yaa Allah ka Qara karemu daga zina, masuyi kuma Allah ka shiryasu
Read More»
Subscribe to:
Comments (Atom)






