Thursday, January 23, 2020

Fateema Habeeb 25

Fateema Habeeb  25



                   na
Jamilu el hussain zazzau



             dedicated to
       Amina baba kaduna



ALLAH KA JIKAN MAHAIFINA, ALLAH KA GAFARTA MISHI, YA ALLAH KA KAI HASKE KABARINSA, ALLAH KASA MUTUWA HUTUCE AGARESHI DA SAURAN MUSULMI BAKI DAYA




Waje kowannen su ya samu ya zauna, principal ya dago kai gami da kallon su rike da biro a hannusa yace to ina jinku meke faruwa ne? bargon lullubar fatima copper yusif ya amsa ya mikawa principal yace sir kalli yadda yaron nan yaje har lodge dinmu yay ma fatima rubutu a jikin mayafin kwanciyar ta,

amsar bargon principal yayi, tsaf ya karanta abinda ke ciki abin ya bashi mamaki, kai ya dago ya bisu da kallo daya bayan daya, sannan yace kuna da tabbacin cewa shiya rubuta?

budar bakin copper kadija tace of course sir, domin yayi irin hakan sau da yawa ni nake kare shi, kawai gajiya nayi shiyasa nake ganin ya kamata nabari a hukunta shi ko zai gane kuskuren sa,

na dan lokaci kadan principal yay shiru, sannan ya dago kai ya kalle su yace ba damuwa ku tashi kuje, hukumar makaranta zatai zama a kanshi, atare su hada baki suce thanks u sir, sannan suka fito daga office din su wuce staff,

principal na kammala abinda ya keyi ya fito, kanshi tsaye ya nufi staff ya kira sajan sunufi class din su habib, suna shiga students duk su mike, yace kar ku damu ku zauna, ina habib sani? hannu habib ya daga yace sir ganinan,

harara sajan ya jefo masa yace stupid come out, kai tsaye habib ya kama hanya ya fito, yana zuwa gabansu sajan ya zabga mishi mari yace wawan banza wuce muje, a gaba su tasa keyar habib zuwa office din principal,

suna shiga su saka shi ya zube akasa, kafin kace wani abu sajan yafara sauke mishi dorina ajiki, kallo principal ya watso mishi yace kyale shi haka, sannan ya kalli habib ya nuna masa mayafin fatima yace meyasa kai wannan rubutun?

dago kai habib yayi ya kalli rubutun, sannan ya sunkuyar dakai kasa, tsawa principal ya daka mishi yace ba dakai nakeyi ba, baza kai magana ba? kadan habib ya dago kai yace sorry sir, ran principal abace yace sorry for what? yace please sajan ci min uban yaron nan, ji kake tas, tas, ganin jikinsa yayi laushi yace barshi haka,

kallo principal ya watso ma habib cikin bacin rai yace idiot go back to your class, sannan ka jira hukuncin da hukumar makaranta zata yanke akan ka, tashi habib yayi cikin tsamin jiki yanufi class din su,

yana fita principal ya kalli sajan yace jeka kiramin vice da admin master kace kome su keyi su bari suzo akwai al amari na ujila, sajan yace ok sir, da sauri sajan yaje ya sanar dasu, cikin hanzari kowannen su ya kamo hanya yazo,

kallo vice ya watso ma principal gami da cewa sir lafiya kuwa? a tsanake principal ya basu labarin duk abubuwan da habib yay ma fatima, nanfa su shiga cancel meeting, daga karshe duk bakin su yazo daya, suka yanke shawarar cewa kawai a kore shi daga school din,




from the experience of jamilu zazzau

WhatsApp  08104550703
Read More»

Fateema Habeeb 24

Fateema Habeeb  24

                    na
Jamilu el hussain zazzau

           dedicated to
     Amina baba kaduna

3 weeks letter,

A kullum soyayyar fatima sake bijirowa habib keyi acikin zuciyar sa, zaune yake watarana a cikin gida yana tunanin ta, kawai zuciyar shi ta rada mishi cewa ya tashi ya tafi lodge din su domin yay tozali da ita ko zuciyar ta sami saukin tunanin da takeyi,

tashi yayi ya debi ruwa ya  shiga bandaki, yana fitowa sami lotion mai kamshi ya shafa, sannan ya canza kaya kai tsaye ya nufi lodge din, ko tsoro babu cikin zuciyar habib kai tsaye yasa kai ya shiga ciki,

yana shiga ya iske duk basa nan dakunan su akulle duk sun shiga cikin gari, yana duba igiyar shanyar dake ciki ya iske kayan fatima tayi wanki, maka ya dauka a jikin wani window ya rubuta, zanyi alfaharin kasancewa tare dake har karshen rayuwa ta, yana gama rubutun ajikin mayafin ta ya mayar da makan ya fito yay tafiyar sa,

6:00pm na yamma fatima su dawo daga cikin gari, suna shiga lodge ta kwashe shanyanta ta shiga dasu daki, bayan sun gama abinci kowa taje tai sallah, sannan su dawo kan abincin suna ci suna fira, zuwa karfe goma su fito atare sukai brush sannan su koma daki su kwanta,

misalin karfe sha biyu na dare a kawo nepa, fatima na farkawa ta gansu acikin haske sun manta basu kashe kwan dakinsu ba,

tana zame mayafin kwanciyar a jikin ta taga wannan rubutun, da sauri ta saki mayafin ta tsandara ihu, a firgice kadija ta farka tana tambayar ta lafiya kuwa?

karar kwan kwasa kofa suji, cikin faduwar gaba kadija tace waye? copper yusif yace mune ihu muji me yake faruwa ne? kai tsaye ta taso ta bude musu kofar su shigo,

watso mata kallo suyi gaba daya suna tambayar ta lafiya kike zabga irin wannan ihun acikin daren nan, bargon ta nuna musu tace ku duba mayafin kwanciya ta kuga rubutun dake ciki,  copper yusif ya tsuguna ya dauka gami da karantawa ya gani,

sannan ya kalle su yace yanzu kunga dare ne, saboda haka abinda nake so daku kowa ya koma daki ya kwanta, idan Allah ya kaimu gobe saimu shiga da bargon school mu nunawa principal, suce ok ba damuwa, kai tsaye kowa ya koma daki ya kwanta,

washe gari da safe bayan sun shirya, copper's sama da biyar su jera tare da fatima zuwa cikin school, suna shiga school din kai tsaye su zame zuwa office din principal,

permission su dauka, yace yes ku shigo, ganin su da yawa yasa principal ya dago kai yace lafiya kuwa? kadan kadija ta saki fuska tace lafiya qalau sir,

from the experience of jamilu zazzau

WhatsApp   08104550703
Read More»

Fateema Habeeb 23

Fateema Habeeb  23

                   na
Jamilu el hussain zazzau

            dedicated to
      Amina baba kaduna

2 days da faruwar hakan har habib ya mance duk nasihar da copper kadija tai mishi, kai tsaye ya kama hanya ya nufi har copper's lodge rike da chalk a hannun sa, yana zuwa ya sami dai dai kofar shiga ya rubuta, u are d only on my heart fatima, yana gama rubutawa yasa kai yay tafiyar shi,

da yawan copper's sun  wuce hankali su baije kan rubutun ba, 5:30pm kadija da fatima su dawo daga cikin gari, suna isowa bakin lodge sukai ido biyu da wannan rubutun, rai abace fatima ta kalli kadija tace kin gani ko? yaron nan idan bansa anci ubanshi ba bazai fita harka taba, da sauri ta shiga ciki taje kiran copper yusif,

ganin haka yasa kadija tai sauri ta samo dosta ta share rubutun, suna fitowa copper yusif ya kalli fatima yace ina rubutun yake? wurgo ma kadija kallo tayi tace wato share wa kikayi ko? kadan kadija ta saki numfashi tace kunga mu shiga daga ciki kawai, ku manta komai ya wuce,

kai fatima ta girgida gami da cizon libs tace zan kama meyin hakan koma wanene, atare su koma cikin lodge din,

washe gari da safe duk suka shirya sanye da kayar bautar kasa a jikin su, domin ranar zasu tafi taro local government secretaria, tafiya su keyi suna dibar fira abin su kadija ta tuna ta mance wani abu a daki,

kallon fatima tayi tace kawa nayi mantuwa, rike min bag dina ki wuce barina koma na dauko, fatima tace ok, da sauri kadija ta kama hanya ta koma lodge, tafiya fatima ta cigaba dayi tana isa cikin school taga jikin wani bangon class an rubuta copper fatima u are d only person I always seeing on my dream,

tana gama karantawa ta girgida kai tace ji dan iska harda nan ma, da sauri ta karisa staff domin ta samo evidence, teachers guda biyu ta kira su kamo hanya tare,

kafin su kariso har kadija ta iso wajen, tana gani ta share rubutun sannan ta cigaba da tafiya, a hanya ta hadu dasu tace lafiya kuwa, ina za kuje haka?

kallo fatima ta wurgo mata tace kema zo muje ki gani ma idon ki, suna karisawa su iske a share rubutun, kallo su watso mata suce ina rubutun yake? shiru tayi jikin ta yay sanyi tace kuyi hakuri ina ganin wani ya goge, amma ba komai koma waye kiyin hakan asirinsa zai tonu, atare su kama hanya su koma cikin school,

9:00am su kama hanya su nufi local government, misalin karfe sha daya su dawo, bayan sun huta kowa ya duba time table ya tafi class din da yake dashi,

class din su habib fatima taje, tana shiga students su mike atare su gasshe ta, tace ku zauna, da sauri class captain ya dauko dosta ya share mata black bord, kai tsaye tafara lesson,

tambaya tayi class yay tsit babu wanda ya sani, hannu habib ya daga, tana gani ta harare shi taki pointing din shi, ta cigaba da lesson dinta, duk tambayar da tayi saiya daga hannu ita kuma taki pointing din shi, domin jikin ta yabata cewa shi yake wannan rubutun,

from the experience of jamilu zazzau

WhatsApp  08104550703
Read More»

Fateema Habeeb 22




Fateema Habeeb  22

                     na
Jamilu el hussain zazzau

            dedicated to
       Amina baba kaduna

ok meyasa kai wannan rubutun? budar bakin sa yace sir gaskiya banji dadin abinda tasa aima same name dina bane, principal yace ok za kaci ubanka,

kallon teachers din nan yayi yace ku bashi kashi, atare su fara tsulan shi, ji kake tas tas tas tako ina, ganin jikin sa yayi laushi principal yace ku kyale shi haka, kallo ya watso mishi yace stupid tashi ka wuce class gobe ka sake, cikin tsamin jiki takwaran habib ya tashi ya koma class din su,

3 weeks da faruwar wannan al amarin, class teacher din su habib ya aike shi staff ya dauko mishi register, yana shiga staff habib ya iske teachers din dake ciki sai famar dibar fira su keyi, fakar idon su yayi ya karisa kujerar fatima, wani littafi ya gani a saman table dinta da sauri ya bude bangon littafin ya rubutu I love u fatima, yana rubutawa ya mayar da sauri ya aje, kai tsaye yaje ya dauki register din ya fita,

12:pm na rana fatima ta dawo staff, tana shigowa ta iske kadija zaune tana hutawa, kallo ta watso mata kawa baki da class ne? kai kadija ta dago su hada ido tace sai zuwa 12:50pm,

bag fatima ta ajiye sannan ta sami waje ta zauna, tana kallon book dinnan taga alamar kamar an taba, domin habib bai mayar dashi inda ya same shi ba, tana budewa taga wannan rubutun, fuska a daure ta nunawa kadija tace kawa kinga abinda wani dan iska yay min ko,

amsa kadija tayi tace mugani me aka rubuta? tana dubawa tai murmushi tace haba to menene don ance I love u? bafa I hate u aka rubuta ba, kai fatima ta girgida tace lallai ne kawa yanzu na fahimci ko kadan bakya son gaskiya,

numfashi kadija taja, tace bahaka bane kawai dai kin kasa fahimta tane, amma dan Allah mubar maganar nan iya mu biyu basai  kowa ya sani ba, domin kina fada za ace habib ne koda bashi ya aikata ba,

ummm aini nama fiso ace shi dinne a farfasa mishi jiki, domin na tsane shi sosai, hannu kadija ta dora a kafadar ta tace naji, amma dan Allah akan wannan kiyi hakuri idan ki sake gani saiki dau mataki koma me zakiyi bazan hanaki ba, numfasawa fatima tayi tace to shikenan, nan suka bar wannan firar suka shiga wata saugar,

ana gab da tashi school kadija taje har class din su habib ta kira shi, a waje su tsaya, tace kaga habib tambayar ka nake so nayi amma banso kai min karya, fuska a sake yace ba damuwa malama yi tambayar ki naji,

tace kaine kaje har staff kayi wa fatima rubutu a bangon littafin tako? nadan lokaci kadan yay shiru sannan ya dago kai yace hakane nine,

tace haba habib meyasa kai haka, shin taya ma akayi ka shigo har cikin staff babu wanda ya ganka? uncle ne ya aike ni staff na dauko mishi register, ina shiga na iske teachers sai dibar fira su keyi duk hankalin su baya kaina, kawai sai nayi amfani da wannan damar na rubuta,

shiru kadija tayi tana sauraran shi, yana gamawa tace tabbas kayi babban kuskure domin da ace wani ya ganka fa? kai ka sani da yanzu wani labarin ake ba wannan ba, saboda haka ina baka shawara kada ka sake aikata irin wannan kaji,

yace zan kiyaye insha Allahu, tace to shikenan Allah yasa, yace amin malama nagode,

from the experience of jamilu zazzau

WhatsApp  08104550703
Read More»

Saturday, December 7, 2019

Fateema Habeeb 21



Fateema Habeeb  21



                    na
Jamilu el hussain zazzau



           dedicated to
     Amina baba kaduna




kallo copper kadija ta watso ma habib, tace masu suna habib ku nawa ne a ss 3? kadan habib ya dago kai yace muna da yawa,

nadan lokaci kadan tai tunani sannan ta numfasa ta kalli principal, tace sir ina ganin ya dace duk wani students mai suna habib a ss3 ya kamata akira shi domin tabbatar da wanda yay wannan rubutun acikin su, domin a tunani na wani na iya rabewa da sunan habib ya aikata hakan,

kadan principal ya numfasa yace bamu ki shawarar da kizo da ita ba, to amma muddin bamu sami wani ba dole shi zai amsa wannan laifin, tabbas kuma hukumar makaranta zata hukunta shi,

dago kai habib yayi yace na yarda, numfashi principal yaja sannan ya kalli displine yace kuje duk ss3 daga A har zuwa C duk wani student mai suna habib ku taho min dashi,

displine yace ok sir, kai tsaye su kama hanya su nufi ss3A, suna shiga students duk su mike su gasshe su, tambaya suyi mutun nawa ne masu suna habib acikin class din nan? ace mutum daya, suce ina shike ya fito, da sauri habib musa ya fito, suka tasa keyar shi su nufi ss3B,

nan dama habib ne kawai mai suna a class din, nan suka fito su nufi ss3C, suna zuwa su sami masu suna habib guda biyu a can, kai tsaye su taso keyar su zuwa office din principal,

suna shigowa duk asa su sukasa guiwar su akasa, muzurai displine yay musu yace kai acikin ku waye ne yaje cikin toilet yay rubutun batanci ga copper?

duk shiru su kayi, wannan ya kalli wannan, wannan ya kalli wannan, tsawa displine ya daka musu yace koba daku nake magana ba? da sauri kowa yace bashi bane, kai displine ya girgida ya kalli kadija yace copper dama na fada miki babu wanda zaiyi rubutun nan face wannan shaidanin yaron,

kallon su yayi yace ku tashi ku koma class, har sun mike zasu fita kadija tace ku dakata, chalk ta dauka taba kowa daga cikin su tace ga black bord nan, inason kowannen ku ya rubuta min malama fatima azzaluma,

amsa su kayi sufara rubutawa daya bayan daya, ana zuwa kan wanda yay rubutun hannunsa yafara rawa, yayi kokarin canza hand write amma ya gagara, ganin yadda ya daburce tace ma sauran ku kukoma gefe kai rubuta mugani,

yana gama rubutawa ta kalli habib tace kaima tashi ka rubuta, mikewa habib yayi ya amsa chalk ya rubuta, kadan tai numfashi sannan tai murmushi, teachers kowa ya zuba mata ido,

kallon yaron nan tayi, tace wannan shi yay wannan rubutun, idan kunaso ku tabbatar kuje ku sake duba wancen rubutun da kyau zaku fahimci abinda nake fada muku,

atare wasu daga cikin su suka koma toilet su duba wancen rubutun, suna dawowa suka sake duba wannan da kyau suce tabbas rubutun shine, a fusace displine ya kalli yaron yafara mishi barazana sai gashi yaron amsa laifin sa cewa shi yayi, kadija tace to kun gani ko? dama tsoron da naji Kennan kada aje a hukunta habib akan laifin da bashi ya aikata ba,

numfashi principal yaja ya kalli Habeeb yace Allah ya kwace ka tashi ka wuce class, yace ma sauran kuma ku wuce, tsawa ya dakawa yaron da yay rubutun yace kai menene cikakken sunan ka? yace Habeeb garba,





from the experience of jamilu zazzau

WhatsApp  08104550703
Read More»

Fateema Habeeb 20



Fateema Habeeb  20



                    na
Jamilu el hussain zazzau



           dedicated to
      Amina baba kaduna




kai tsaye ya koma office din principal ya shaida mishi yadda su kayi da fatima, principal yace to shikenan tunda ta yafe komai ya wuce, saide kaja mishi kunni saboda kujewa faruwar haka nan gaba, malam sani yace insha Allahu, nan sukai sallama ya fito ya dauki mashin dinsa ya nufi gida,

murja ya iske zaune a dokin kofa rike da kofin kunu a hannu tana jiran dawowar shi, sallama yayi, ta amsa tace megida ka dawo? yace eh, kadan ya dan gusa kusa da ita ya samu guri ya zauna,

labarin duk abubuwan dasu faru ya kwashe ya bata, cike da mamaki ta girgida kai tace kai amma gaskiya habib be kyauta ba, amma duk da haka hukuncin da suka masa yayi tsauri da yawa,

wurgo mata kallo yayi yace to ai maganin sa Kennan, tashi ki miko min sakon nan nazo na wuce kasuwan nan, tace to megida,

1:30pm a tashi daga school, habib na shigowa gida ko zama beyi ba murja ta rufe shi da fada, wawan banza dama soyayya muka tura ka kayi a school din?

banda rashin hankali irin naka duk yara matan dake school din babu wacce tai maka sai malamar ka, ga yaran makota nan duk baka ga wacce kakeso ba har saida kaje ka jawo ma kanka fitina, duk fadan da murja take mishi shiru yayi baice komai ba harta gaji ta daina,


A bangaren kadija kuwa suna komawa lodge kallo ta watso ma fatima, tace a gaskiya kawa banji dadin abinda kiyi ma taohon nan ba, yatsine fuska tayi gami da kada kai tace dansa yaja masa,

kadija tace naji amma koba komai ai ya haifeki, fatima tace yadai haife shi amma bani ya haifa ba, kinga kadija barina taka miki birki naga akan wannan al amarin kina son ki rikayi min shishshigi, gaskiya idan baki bari ba zamu sami matsala, numfashi kadija taja tace to shikenan Allah ya baki hakuri,


2 weeks da faruwar haka, wani student yaje har toilet din malamai ya rubuta copper fatima ke jahila ce, kuma azzaluma mara tunani, jaka ma tafiki hankali, nine habib daga ss 3,

11:00pm na ranar copper yusif ya dauki buta ya nufi toilet din domin ya zaga, ya gama lalurar sa zai fito yaci karo da wannan rubutun, da sauri ya nufi staff ya sanar da duk malaman dake ciki,

gaba yayi duk suka biyo shi abaya, suna zuwa kowa ya ganema idonsa, kafin kace wani abu har ansami wani daga cikin su yaje ya sanar da principal, cikin bacin rai principal yace kuje ku duba ku gani idan yaron yazo school ku taho dashi,

kusan malamai biyar su nufi class din su habib kowa rike da bulala a hannu, suna shiga class din cikin uban kowa ya duri ruwa, displine yace ina habib sani?

mikewa habib yayi yace sir gani nan, yace fito dan ubanka, tashi guda hantarsa ta kada cikin kyarmar jiki ya fito, kai tsaye su tasa keyar shi zuwa office din principal, dai dai lokacin kadija na cikin wani class tana lesson taga an wuce dashi, da sauri ta fito ta bisu abaya,

suna shiga principal ya watso mishi kallo yace sa guiwar ka akasa, da sauri habib yay biyayya yay kasa, cikin bacin rai yace mishi wato kai saboda iskanci har cikin toilet dinmu kaje ka rubuta kalaman batanci ga copper dun tace bata sonka ko?

fuska cike da kwalla habib yace sir wallahi bani bane, principal yace oh bazaka fadi gaskiya ba Kennan? yace sir na rantse maka banma san anyi ba, principal yace to shikenan tunda bazaka fadi gaskiya ba barina sa abaka kashi,  shiru habib yayi idanuwan sa duk su cika da kwalla,

murmushi displine yayi yace yaro kenan, tun ban fara cin ubanka ba harka fara kuka, tsawa ya daka mishi yace tashi muje, kadija tace kunga ku dakata, yana da kyau ku tabbatar cewa shiya aikata kafin ku hukunta shi, displine yace to mun baki dama ya kike so ayi?



from the experience of jamilu zazzau

WhatsApp  08104550703
Read More»

Fateema Habeeb 19


Fateema Habeeb  19



                    na
Jamilu el hussain zazzau



     
            dedicated to
       Amina baba kaduna





suna cikin magana sai ga malam sani ya shigo, kallo ya watso musu yace lafiya kuwa? rigar habib ta daga mishi tace megida kalli jikin yaron nan sai kace wanda yay sata,

nadan lokaci kadan malam sani yay shiru, sannan yace to kin tambaye shi abinda yayi akai mishi hakan? eh mana, ya fadamin tuk akan fashin makarantar da yayine kwana ki shine har yanzu cin zalin bai ishesu ba,

paper din habib ya mika mishi, malam sani ya amsa ya karanta, sannan ya dago kai ya kalli murja yace cewa suyi suna bukatar ganina, kinga idan naje koma menene zasu min bayani ai, tace to shikenan Allah ya kaimu, yace amin,

waje habib ya samu ya baje a tabarma, da sauri murja ta dora mishi ruwan zafi domin ya gasa jikin shi, sannan taje ta kawo mishi abinci da ruwan sha, ranar babu inda habib ya fita,

washe gari da safe habib ya tashi yay shirin school, yana gama karyawa malam sani yace to dauko jakar ka muwuce, kan mashin ya dauki habib sunufi school din,

suna isa ya kafe mashin din, sannan ya tasa keyar habib zuwa office din principal, malam sani na shigowa principal ya nuna mishi kujera yace ga wuri nan zauna,

bayan sun gaisa yace naga yaro da sako shine na biyo baya, numfasawa principal yayi yace malam sani yaron ka ya tabka babban kuskure, amshi wannan takardan ka karanta kaga abinda ke ciki,

amsa malam sani yayi ya karanta tsaf, cike da mamaki ya kalli habib yace kai ka rubuta wannan? ba gardama habib yace eh, shiru malam sani yayi sannan ya girgida kai yace lallai yaro ka girma, sannan ya kalli principal yace malam buhari dan Allah kuyi hakuri,

girgida kai principal yayi yace malam sani ai bani zan yanke hukunci akan wannan al amarin ba, hukumar makaranta da ita wacce akayi wa laifin su suke da hurumin yafe masa, abin ya batawa malam sani rai sosai, cikin zafin rai ya fito daga office din principal ya nufi staff,

yana shiga ya samu wani teacher yace mishi nine mahaifin yaron nan da yayiwa malamar shi wasika jiya, nazo ne domin na roketa tayi hakuri, teacher din yace tana can tana koyarwa saide kadan jira ta dawo tukun,

malam sani yace ba damuwa, waje ya samu ya zauna, zuwa can sai gata ta shigo ita da kadija, nuna mishi ita teacher din yayi yace yauwa baba  gatacan ta dawo, itace mai bakin hijabin can,

da sauri malam sani yaje ya sameta yace malama barka da fitowa, kallo ta watso mishi tace old man meke faruwa? tana fahimtar cewa mahaifin habib ne saita juya harshenta na nufanci ganin cewa yana jin turanci, saboda batason ta saurare shi, domin batason ta yafema habib ita burinta kawai a kore shi daga school din,

ganin haka yasa malam sani ya juya zuwa gurin teachers din dake cikin staff din yace dan Allah kusa mana baki ko zata hakura,

tana jin ya fadi haka taja tsaki ta fita daga cikin staff din, ganin haka yasa kadija tabita  da sauri tace haba kawa meyasa kike irin wannan, ya kamata ki dawo cikin hankalin ki, wannan abinda kiyi sam bai dace ba,

cikin fushi fatima ta kalli kadija tace dakata min malama, me kike nufi dana dawo cikin hankalina? ok kina nufin yanzu bani da hankali kenan,

suna cikin haka malam sani ya kariso wajen ya kalli fatima, yace yarinya ki dubi tsufana da yadda nake rokon ki kiyi hakuri kuskure ne insha Allahu hakan bazai kuma faruwa ba,

waigowa fatima tayi ta nuna malam sani da yatsa tace naji na hakura,  amma kaja masa kunni ya tabbar hakan bai kuma faruwa ba,

malam sani yace nagode yarinya Allah ya miki albarka, juyawa yayi zuwa cikin staff yay sallama da sauran malaman sannan ya fito,





from the experience of jamilu zazzau

WhatsApp  08104550703
Read More»

Fateema Habeeb 18

Fateema Habeeb  18



                    na
Jamilu el hussain zazzau




              dedicated to
        Amina baba kaduna




misalin karfe goma na safe lokacin kowani students na class, kai tsaye fatima ta fito daga  staff ta nufi office din principal,

permission ta dauka, principal yace yes shigo, fuskanta a sake ta shigo ta samu waje ta zauna, kallo principal ya watso mata yace copper meke faruwa?

hannu tasa a jaka ta dauko wannan wasikar ta mika mishi, principal ya amsa ya karanta, yana gama karantawa ya dago kai ya kalle ta yace copper waye yay miki wannan wasikar?

tace sir wani student ne, kuma na waye shi, yace idan kin ganshi zaki iya nuna shi? tace yes sir, yace ok tashi muje, kai tsaye su zame staff principal ya kwaso teachers sama da goma kowanne rike da bulala a hannu sunufi class din su habib,

suna shiga class din students kowa ya mike, tashi guda cikin kowa ya duri ruwa, cikin zafin rai principal yace waye habib sani? mikewa habib yayi yace gani sir, yace come out, a tsorace habib ya kama hanya ya fito, tsawa principal ya daka mishi yace kai da waye kuje copper's lodge jiya?

waigawa habib yayi ya kalli abdurrahaman yaga sai famar kyarma ya keyi idanuwan sa duk sun ciko kamar zeyi kuka, yace sir bezo ba, principal yace ok wuce muje, agaba su tasa shi zuwa staff, suna zuwa habib yasa guiwar sa akasa,

kallo principal ya watso mishi yace waya rubuta wannan wasikar? habib yace nine, yana fadin haka principal ya wanka mishi mari yace idiot,

kallon teachers din nan yayi yace ku bashi kashi, ji kake tas tas tas duka kawai tako ina, ko kuka habib ya kasayi sai ninshi kawai, ganin jikin sa yayi laushi principal yace ku barshi haka, ya kalle shi yace toya kana kan bakar ka koka saki?

dago kai habib yayi yace sir har yanzu ina sonta, principal yace ashe be dakuba ku cigaba, tas tas su cigaba da tsulan shi, principal yace ku dakata, kallo principal ya sake watso mishi yace toya ka janye ko kuwa?

kai habib ya dago ya kalli fatima yace I love u, jin haka yasa finance ya kalli principal yace sir ina ganin bayin kansa bane, ba mamaki akwai abinda ke damun sa, yana da kyau koda iyayen shine a bincika aji ko yana da tabin hankali, principal yace ok bari mu gwada yin hakan mugani,

kallon habib yayi yace tashi muje, kai tsaye ya tasa shi agaba zuwa office din sa, paper ya samu yay rubutu yace amshi wannan ka wuce gida yanzu ka kaima mahaifin ka,

amsar paper din habib yayi ya fito, jikin wata bishiya ya samu ya zauna yana huta gajiyar dukan da yasha, ana tashi school habib yabi ayarin students sunufi gida,

tafiya su keyi class mate din shi kowa na fadin albarkacin bakin sa, wannan yace gaskiya habib kayi rashin hankali, wannan yace gaskiya baka kyauta ma kanka ba, murmushi habib yayi yace bazaku gane bane, Ishaq din class din su yay dariya yace aikai daka gane gashinan an baka sakamakon ganewar, haka su cigaba da tafiya har suka isa gida,

habib na shiga gida murja ta ganshi a yamutse kamar wanda ya fito daga prison, matsowa kusa dashi tayi taga rigarsa har tana yagewa tsabar duka,

daga rigar  tayi taga bayansa yayi rudu rudu ga shaidar bulala, har tana hawaye tace Habeeb waya maka irin wannan hukuncin,

numfashi yaja yace umma su nada yawa, tace to laifin me kayi haka? ko dai tun akan wannan maganar ta kwana kine?




from the experience of jamilu zazzau

WhatsApp  08104550703
Read More»

Saturday, November 30, 2019

Fateema Habeeb 17

Fateema Habeeb  17



                     na
Jamilu el hussain zazzau



     
             dedicated to
       Amina baba kaduna




malama nima banyi kaina bane, domin tun ranar dana ganta zuciya ta ta kamu da sonta, tun a wancan lokacin nai kokarin kawar da soyayyar da karfi amma abin yafi karfi na, domin a sanadiyar afkawa soyayyar ta har matsala na samu da iyayena, baya ga nan na samu matsala da malamai na, na kuma amshi horo da azabtarwa iri daban daban,

saboda haka tunda na riga na furta na gummace na mutu akan na janye abinda ke zuciya ta, tace oh yanzu habib kana nufin bazama ka janye wannan maganar bama kenan? yace wallahi malama bazan iya ba, idan na janye mutuwa zanyi, saboda haka na dauki damarar jure duk wata wahala da zata biyo bayan yin hakan,

jin wadan nan jerin kalaman daga bakin habib yasa jikin copper kadija yay sanyi, tashi guda tausayin shi ya kamata, tace kabari zan sameta a tsanake na fahimtar da ita duk yadda muyi zan sanar dakai, yace nagode saida safe, tace Allah ya kaimu,  kai tsaye habib ya kama hanyar gida, ita kuma ta koma cikin lodge din,

copper kadija na shiga kai tsaye taje daki ta iske fatima, kusa da ita ta samu waje ta zauna agefen katifa, tace kawa inason muyi magana akan habib, fatima tace umhum ina jinki, kallo kadija ta watso mata tace a zahirin gaskiya bazan boye miki ba yaron nan ya kamu  tsananin soyayyar ki, game da labarin irin halin daya shiga akan soyayyar ki yasa jikina yayi sanyi sosai, tabbas na tausaya mishi,

kallo fatima ta jefo mata, tace yanzu me kike nufi? numfasawa kadija tayi tace ki taimaka ki ceto rayuwar shi, yatsine fuska fatima tayi tace me kike nufi dana ceto rayuwar shi? kadija tace ina nufin ki amshi soyayyar shi,

rai abace fatima tai girgida kai tace kin raina min hankali, in banda kin raina min wayau ni zaki kalla kice nai soyayya da students dina, wanda na tsere mishi ta kowani fanni,

numfashi kadija taja, sannan ta girgida kai tace wannan ba rainin wayau bane kawai zan iya cewa wani al amari ne daga ubangiji, domin shi Allah yana iya sarrafa al amarin sa takowani fanni kuma a lokacin da yaga dama, idan zaki tuna tarihin mazon Allah (s a w) lokacin da uwar muminai nana kadija ta aure shi aita girme shi sannan ta fishi arziki, saboda haka a tunanina ma yin hakan koyi da sunna ne,

buder bakin fatima tace ai naga kema mace ce, idan da gaske ki keyi kin tausaya mishi kamata yayi ki amince ki aure shi, kai kadija ta dago ta kalle ta, tace kar ki manta tare ya ganmu amma ya zaba cewa ke yake so,

cikin fushi fatima tace to bana son shi, ko ana so dolene? kuma na rantse miki saina sa an hukunta shi, domin ya zame mishi darasi nan gaba, kadija tace ba damuwa Allah ya taimaka, tana fadin haka ta tashi ta fita,

washe gari da sassafe abdurrahaman ya dauki waya yakira habib, habib na dubawa ya daga gami da girgida kai, abdurrahaman yace hello abokina ya akayi ne? numfashi habib yaja yace normal, abdurrahaman yace wai jiyan nan ya kuka kare dasu ne? habib yace abinda kasani miye kuma na tambaya,

murmushi abdurrahaman yayi, yace malam habib kenan yanzu menene mafita? numfashi habib yaja, yace yadda Allah yay damu haka za ayi,

dariya abdurrahaman yayi, yace gaskiya abokina ina baka shawara kada kaje school yau, domin komai na iya faruwa, numfashi habib yaja, yace zanje domin na tabbatar ba kashe ni za suyi ba, abdurrahaman yace babu maganar kisa amma zasu kashe ma fatar jiki,

tsaki habib yaja ya kashe wayar shi ya koma ya cigaba da baccin sa, gari na gama wayewa ya tashi ya shiga wanka, yana fitowa ya shafa mai ya saka uniform, yana gama break fast ya dauki jaka yanufi school,




me karatu ya kake gani zata kaya, domin sanin hakan sai kayi kokari ka nemi cigaban labarin




from the experience of jamilu zazzau

WhatsApp  08104550703
Read More»

Fateema Habeeb 16

Fateema Habeeb  16



                      na
Jamilu el hussain zazzau



             dedicated to
       Amina baba kaduna




5:00pm habib ya debi ruwa ya shiga wanka, yana fitowa ya shiga daki ya sami versiline dinsa mai kamshi ya shafa, sannan ya sami black trouser da red t shirt ya saka, explorer perfume ya fesa sannan ya sauki takalmi ya saka ya fito, kai tsaye ya nufi gidan su abdurrahaman,

yana zuwa ya iske abdurrahaman zaune a kofar gida yana jiran sa, yace sorry na bata lokaci ko? abdurrahaman yace lallai kam ka kusa makara, murmushi habib yayi yace to musa kai kawai,

tafiya suke suna fira kai tsaye su nufi copper's lodge, a bakin kofa su tsaya su rasa wanda zai shiga yakira musu ita, ana cikin haka sai ga copper yusif ya dawo daga cikin gari, da sauri su taso suzo su gasshe shi, yace wa kuke nema ne? suce copper fatima, yace ok bari nai muku magana da ita, suce thanks sir,

copper yusif na shiga ya iske fatima zaune acikin copper's suna fira, kallon ta yayi yace fati kinyi baki, da sauri ta watso mishi kallo itama, tace baki? murmushi yayi yace students dinki ne, tace oh shine zasu tsaya a waje, copper yusif yace to kila ko kunyar shigowa su keji tashi kije ki shigo dasu,

yunkurawa fatima tayi ta shiga daki ta dauko hijabi ta saka, kai tsaye ta nufi waje, tana fita ta iske su a tsaye, tace oh kune? fuska abdurrahaman ya saki yace wallahi kuwa, bayan sun gaisa tace lafiya ko? kadan abdurrahaman ya sosa kai yace qalau, dama munzo fada miki wani sako ne,

tace ok ina jinku, hannu abdurrahaman yasa cikin aljihun sa ya dauko wannan wasikar daya rubuta ya mika mata, yace ga wannan sakon dake tafe damu yana ciki, 

kallo ta watso mishi tace menene aciki? yace kar ki damu ki bude zaki gani, idan kin karanta habib zaki bama amsa, yana fadin haka ya kalli habib yace abokina minti daya ina zuwa, da sauri ya lallaba yaje jikin wata bishiya ya buya domin yaga abinda zai faru, fatima na budewa taga rubutu kamar haka,

   
         aminci agareki

dafatan kina cikin koshin lafiya kamar yadda nake, a gaskiya fatima tun ranar da Allah yasa nai tozali da kyakkyawar surar ki Allah ya jarabce ni da tsnanin sonki, wannan dalilin yasa nazo domin bayyana miki, ina mai fatan zan sami masauki acikin zuciyar ki, 

        daga masoyinki na har abada habib sani ss3B,

tana gama karantawa ta dago kai ta kalli habib tace waya rubuta wannan wasikar? numfasawa habib yayi yace nine, tun kafin ya rufe baki ta falla mishi mari, tace stupid baka da hankali ne, koka fara shaye shaye ne? idiot ni zaka dubi tsabar idona kace zakai soyayya dani,

da sauri ta koma cikin lodge din ta sanar da sauran copper's abinda ke faruwa, da sauri suka dungumo su fito domin suga wani students ne haka, suna fitowa su iske habib ko motsawa daga wajen da yake tsaye beyi ba,

kallon shi copper yusif yayi yace kai kayi wannan abin? kai habib ya daga yace eh, yusif yace oh dama abinda ya kawo ku kenan? shiru habib yayi yana kallon su kowa na fadan albarkacin bakin sa,

copper yusif yace baku da hankali, amma zakuyi nadamar abinda ku aikata, kusa da habib copper kadija ta matso takira copper yusif tace kunga ku mishi hakuri yanzu, idan ya sake saiku dau mataki,

kai copper yusif ya girgida yace no, bawani hakurin da zatayi dolene ya fuskanci hukunci domin nan gaba ya zame mishi darasi,

can gefe copper kadija taja habib tace mishi meyasa kai haka? hawaye ne suka fara zuba daga idanuwan sa yafara magana cikin rawar murya,




Domin samin littafin daga na daya zuwa inda mu tsaya saika tuntubeni ta wannan number dake kasa,



from the experience of jamilu zazzau

WhatsApp  08104550703
Read More»

Friday, November 29, 2019

Fateema Habeeb 15

Fateema Habeeb  15



                     na
Jamilu el hussain zazzau


       dedicated to
   Amina baba kaduna



Habeeb na karisawa jikin katuwar bishiyar nan ya hau ya sauko da jakar sa dake gurin, daya bayan daya ya fara kallon hotunan fatima, yana gamawa ya mayar ya aje, duk abinda ya keyi abdurrahaman na makale ajikin wata bishiya yana kallon shi,

habib na mayar da jakar ya kama hanya ya nufi cikin school, ganin yayi nisa abdurrahaman ya fito daga wajen da yake, kai tsaye yaje ya hau bishiyar ya sauko da jakan,

bude wa yayi domin yaga abinda suke ciki, yana budewa yaga pictures din copper fatima ne aciki masu kyau tare da kalaman soyayya, kallon su yafara yi daya bayan daya, a bangaren habib kuwa harya kusa shiga cikin school zuciyar shi ta bashi cewa ya koma wajen jakar nan, kawai ya biye mata kai tsaye ya juyo,

tun daga nesa ya hangi abdurrahaman rike da hotunan nan yana kallo, harya iso wajen abdurrahaman baisan ya dawo ba, kadan habib yaja numfashi yace sannu da aiki,

a tsorace abdurrahaman ya zubar da hotunan ya waigo, yana waigowa yaga ashe habib ne ya dawo, yace oh dama baka wuce ba? habib yace ok dama jira kake na wuce kenan?

kai abdurrahaman ya girgida yace aa, habib yace tome ya kawo ka nan? abdurrahaman yace dama zuwa nayi naga wajen da kake zuwa kana hutawa,

murmushi Habeeb yayi, yace yaro nasan meya kawo ka saboda haka barina ja maka kunni, kada ka sake kaba wani wannan labarin, karfin hali abdurrahaman yayi yace haba ai baka isa ba wallahi, domin ina tashi daga nan gidanku zanje na fadawa maman ka, kaga yanzu shikenan zata san abinda ke damun ka,

cikin bacin rai habib ya kalle shi yace haka kace ko? tabbas saina fada musu, domin babu abinda zai hanani fada, kai habib ya girgida yace jikinka ko zai fada maka,

tsimagiya ya dauko ya tunkaro abdurrahaman da ita, ganin haka yasa abdurrahaman yay dariya yace matsala ta dakai bakasan wasa ba wallahi, jin haka yasa habib ya yar da tsimagiyar ya samu waje ya zauna,

kallon abdurrahaman yayi yace abokina tunda Allah yasa yanzu kasan abinda ke faruwa menene shawara? murmushi abdurrahaman yayi yace shawarar kenan kawai ka fito fili ka fada mata cewa kana sonta koma menene zai faru ya faru,

kai habib ya girgida yace wannan ba shawara bace, ko so kake akara azabtar dani? abdurrahaman yace bazata bari akara azabtar dakai ba muddin ta amince, habib yace to naji, idan kuma bata amince bafa?

kai abdurrahaman ya dago yace kar ka damu ni nasan yadda za ayi ta amince, habib yace ok, toya zamuyi mu tunkare ta?

abdurrahaman yace kaga kabar komai agurina zuwa nan da gobe, murmushi habib yayi yace kai amma gaskiya nayi matukar farinciki da zuwan ka,

tattara hotunan habib yayi ya mayar acikin jakar ya hau bishiyar ya sagale sannan ya sauko su kama hanya su koma cikin makaranta,

washe gari suna zaune a cikin class habib ya kalle shi yace ya maganar mu? abdurrahaman yace ban manta ba ai, amma ba'a school zamu fada mata ba kabari sai an tashi sai muje har copper lodged din mu sameta, habib yace ok Allah ya kaimu,

jim kadan abdurrahaman ya yagi wani fallen paper ya rubuta duk wasu bayanai dasu dace su fada mata, yana gamawa ya ninke ya saka a aljihu,

ana tashi school yace ma habib zuwa yamma idan ka shirya saika biyo ta gidanmu mu wuce, Habeeb yace ok ba damuwa sai anjiman,



Hammm me karatu shin ya kake gani, zata iya amince wa kuwa? domin tabbatar da hakan sai kuyi dakon cigaba,



from the experience of jamilu zazzau

WhatsApp  08104550703
Read More»

Fateema Habeeb 14

Fateema Habeeb  14



                     na
Jamilu el hussain zazzau



             dedicated to
        Amina baba kaduna




Washe gari da sassafe habib ya shiga wanka, yana fitowa yay shirin school, sannan ya fito ya karya, jaka ya dauka zai fita malam sani ya harare shi yace idan kaso kar kaje school din ka wuce wani wajen,

kai tsaye habib ya kama hanya sai school, yana isa ya zame class,

displine na zuwa ya wuce wajen aikin da yasa habib domin ya duba ya gani ko yayi, yana zuwa ya iske habib ya gama aikin tsaf, girgida kai displine yayi yace lallai yaron nan yakai tantiri ace mutum ya gummace yay ta shan duka sai kace jaki, kai tsaye ya wuce office din principal yay mishi bayani cewa sir babu inda banyi da yaron nan ba, amma yaki fadamin wajen da yake zuwa,

principal yace kar ka damu jeka abinka ni nasan yanda zanyi dashi, domin naci uban wanda suka fishi gagara, ana tashi break principal yaje har class din su habib ya taso shi agaba zuwa office din sa,

kallo ya watso mishi yace sa guiwar ka akasa, da sauri habib yasa, yace inason kai min bayanin wajen da kake zuwa baka son zuwa school, domin kaga wannan yawon da kakeyi kanka kake zalunta,

shiru habib yayi yaki magana, tsawa principal ya daka mishi yace ba dakai nake magana ba? yace sir ba inda nake zuwa, murmushi principal yayi yace wato har yanzu baka daku ba kenan tunda kaki bayani,

rai abace principal ya kalle shi yace tashi ka kama kunninka awajen, ba gardama habib ya tashi ya kama, principal yay ta aikin shi har ya manta dashi, zuwa can hawaye suyi ta zubo masa kafafuwan sa sukai tsami ya yanke jiki ya fadi,

jin karar faduwar sa yasa principal ya dago dakai ya kalle shi yace ubanwa ya tashe ka? bulala ya dauko yafara tsula mishi, yana fadin dan ubanaka fadamin ina kake zuwa bakasan zuwa school, ihu kawai habib keyi yana fadin kayi hakuri malam babu gurin da nake zuwa,

jin haka yasa principal yace stupid kawai, tashi ka wuce class, da kyar habib ke tafiya, kai tsaye ya koma class,

bai jima da fita daga office din principal ba sai ga mahaifin sa yazo, bayan sun gaisa principal yay ma malam sani bayanin duk irin punishment din da suyi ma habib amma yaki fada musu wajen da yake zuwa, malam sani yace to ba damuwa ku kyale shi nagode, hannu ya bashi sukai sallama ya kama hanya ya koma,


5:pm malam sani ya dawo daga kasuwa, dai dai lokacin habib na zaune a tsakar gida rike da wani karamin littafi yana karatu, kallo ya watso mishi yace wato kaki musu bayani ko? na sake jin ance baka zuwa kagani nida kaina zan casa ka, shiru habib yayi baice komai ba,

washe gari Habeeb na gama shirya wa zai fita murja tace to habib dan Allah ka mayar da hankali kaji, yace to, tace a dawo lafiya, yana fita kai tsaye ya wuce school,

yana shiga class ya ajiye jakarsa ya fito, kai tsaye yanufi bayan gari wajen daya ajiye hotunan fatima, tun daga nesa abokin shi abdurrahaman ya hange shi, da sauri ya kama hanya ya bishi abaya,

zuwa can habib yaji kamar ana biye dashi, da sauri ya waigo  ya duba, abdurrahaman kuma yay sauri ya boye a jikin bishiya, ganin baiga kowa ba yasa ya cigaba da tafiya, abdurrahaman ya fito ya cigaba da binsa,



from the experience of jamilu zazzau

WhatsApp  08104550703
Read More»

Wednesday, November 27, 2019

Fateema Habeeb 13


Fateema Habeeb  13



                      na
Jamilu el hussain zazzau




           dedicated to
     Amina baba kaduna




kallon habib principal yayi, yace jeka kiramin malamin dake kira muku rijista, da sauri habib yaje yakira malam ayuba su dawo tare,

kallon malam ayuba principal yayi, yace shin yaron nan na zuwa school? nadan lokaci kadan malam ayuba yay shiru, sannan ya girgida kai yace gaskiya ya kwana biyu bezo ba, jin haka yasa malam sani ya kalli habib cikin bacin rai yace to ina kake zuwa?

shiru habib yayi yaki magana, ganin haka yasa   malam sani yace ma principal malam buhari inason kuba yaron nan kashi har saiya fada muku gurinda yake zuwa, yana fadin haka ransa abace ya tashi ya wuce,

tsawa principal ya dakawa habib, yace idiot sa guiwar ka akasa,

sallama suji, copper yusif ne ya shigo yace sir akwai chalk anan kuwa? principal yace eh akwai, na staff yakare ne? copper yusif yace yes sir, principal yace ok kwasa da yawa katafi dashi, ya diba zai fita principal yace copper idan kaje kace ma displine yazo da sauri inason ganin shi, yace ok sir, yana zuwa ya fadama displine, da sauri displine yabar abinda ya keyi ya kama hanya,

yana shigowa yace gani sir, principal yace ok abinda nakeso dakai kaje da yaron nan kabashi kashi sosai har saiya fada maka gurinda yake zuwa baison zuwa school, displine yace ok sir, kallon habib yayi yace tashi muje,

agaba ya tasa shi zuwa office din shi, suna shiga yace sa guiwar ka akasa  dan ubanka, da sauri habib yay nildown, displine ya kalle shi yace to zaka fadamin ne ko saina sosa maka baya?

kadan habib ya dago kai yace babu inda nake zuwa, dariyar mugunta displine yayi yace yaro kenan, cire riga dan ubanka, a tsorace habib yacire rigar sa domin yasan halin displine din, ya rage daga shi sai singlet,

ko tausayi babu displine yay ta tsala masa dorina yana cewa zaka fadamin ko kuwa? nin shi kawai habib ya keyi yakasa magana, kafin kace wani abu yayi masa rudu rudu da jiki, duk dukan da habib yasha baisa ya fadi komai ba,

ganin haka yasa displine yace yaro idan kasan wata bakasan wata ba, fatanya ya dauka yace tashi muje, tsakiyar rana ya fita dashi ya nuna mishi wani katon fili cinkushe da ciyawa, yace kaga duk girman wajen nan kai zaka nome shi duka idan baka fadamin gurinda kake zuwa ba, ya mika mishi fatanyar yace gashinan fara nizan wuce office idan ka shirya fadamin saika ajiye fatanyar kazo office ka sameni,

dukawa habib yayi ya dau fatanyar ya dukufa noman ciyawa ko hutawa beyi, har lokacin tashi yayi displine bezo ya sallame shi ba, haka students kowa ya shiga wuce wa yana kallon shi, har students kowa ya gama wuce wa gida sai shi kadai ya rage yana ta famar aiki,

zuwa can displine yazo domin ya duba ya gani ko habib yayi aikin da yasa shi, yana zuwa ya taras habib yayi aikin tas  abin ya bashi mamaki, dariya yayi yace yaro kenan, wato kai dan taurin kai ko? ba damuwa, yanzu zaka fadamin ne kokuwa?

shiru habib yayi kamar ba dashi ya keyi ba, dariyar mugunta displine ya saki gami da nunawa habib wani katon fili yace tunda kace kai kangararre ne to yau anan zaka yini, dauki fatanya ka cigaba da aiki,

dukawa habib yayi ya dauki fatanyar ya nufi gurin, murmushi displine yayi yasa kai ya kama hanyar gida, duk a tunanin sa habib zai kira shi ya fada mishi, ko dago kai habib beyi ba ya cigaba da aikin,

duk school kowa ya watse, ya rage sai shi kadai ga yunwa ga gajiyan aiki, ga kuma zafin rana dake damunsa da kuma zafin dukan daya sha, sai misalin karfe biyar na yamma ya gama aikin,

yana gamawa ya dauki rigarsa ya saka yana tafiya da kyar yanufi gida, murja na zaune a inuwa tana hutawa habib ya shigo gida wujiga wujiga, tsabar tausayi har tana hawaye, tace habib bansan lokacin daka fara gagara ba, yanzu kaki fada musu gurinda kake zuwa ka gwammace aita dukan ka kamar jaki ko?

shiru yayi bece komai ba yasami waje ya zauna, kai tsaye murja ta tashi ta dauko mishi abincin sa,

6:00pm malam sani ya dawo daga kasuwa, yana shigowa ya iske habib ya baje  a tabarma yana huta gajiyar horon da yasha, hararan shi yayi yace shasha shan banza mai kunin kashi, mu zuba nida kai muddin kace gagara zakayi ni kuma zan cigaba da basu umarni suna baka kashi, a ranar habib yakasa zuwa ko ina saboda wahalar da yasha,




from the experience of jamilu zazzau

WhatsApp  08104550703
Read More»

Fateema Habeeb 12



Fateema Habeeb  12



                      na
Jamilu el hussain zazzau



            dedicated to
       Amina baba kaduna




2 weeks letter, habib ya dauke kafa da zuwa school, kullum yay shirin school saiya zame can bayan gari gurinda ya ajiye hotunan fatima, bashi da aikin daya wuce zana hotunan ta da kuma jera baitocin soyayya,

ganin kwana biyu baizo school bane yasa abdurrahaman yaje har gidan su domin ya duba yaga ni ko lafiya yasa be zuwa,

yana shiga gidan ya iske murja zaune tana wanke wanke, sallama yay mata ta amsa,  tace malam abdul yau kaine agidan namu? yace eh umma, aciki ladabi ya gasshe ta, yace dama nazo duba habeeb ne,

da sauri murja ta dago kai ta dube shi dakyau tace wani habib kuma? shida ya wuce school tun  dazu, kai abdurrahaman ya girgida yace umma habib baizo school yau ba, hasalima ya kwana biyu bai zuwa, wannan dalilinne ma yasa nace bari nazo na duba nagani ko bashi da lafiya ne,

jin wadan nan jerin bayanan na abdurrahaman ya batawa murja rai sosai, kallo ta sake watso mishi, tace kaga abdul dan Allah kafada min gaskiyar abinda kasani,

rantsewa abdurrahaman yayi, yace wallahi umma habib yakai kusan sati biyu rabon shi da school, kuma a zahirin gaskiya bansan gurin da yake zuwa ba, murja tace nagode yaro jeka abinka zai dawo gidan zai fada mana gurin da yake zuwa, abdurrahaman yace to sai anjima, kai tsaye ya kama hanya ya koma school,

1:30pm atashi daga school, kai tsaye habib ya kama hanya yabi bayan dalibai yanufi gida kamar wanda yaje school, yana shiga gida ko zama baiyi ba murja ta daka mishi tsawa tace daga ina kake? yace daga school nake, tace rufe min baki makaryaci, dazun nan abokin ka yazo neman ka, yace kusan sati biyu kenan baka zuwa school din, shin ina kake tafiya?

kai habib ya dago yace wallahi karya ya keyi kullum sai naje, tace to shikenan bari mahaifin ka ya shigo na sanar dashi, daki habib ya shiga, tashi guda zufa yafara keto mar yana tunanin abinda zai biyo baya muddin mahaifin shi yasan bai zuwa school,

yamma nayi malam sani ya dawo daga kasuwa, kamar kullum murja taje ta tarbe shi ta kawo mishi ruwa mai sanyi da abinci, bayan ya huta ta kwashe labarin da abdurrahaman ya kawo mata tsaf ta fada mishi, nadan lokaci kadan malam sani yay shiru yana mamaki, sannan ya numfasa yace to shikenan tunda yace karya ne kibari gobe zan tasa keyarsa agaba muje makarantar domin na tabbatar da gaskiyan lamarin, tace to megida Allah ya kaimu, yace amin, sannan suka shiga wata firar,

washe gari da safe habib na gama shiryawa malam sani ya dauke bisa yamaya din shi sai school din, suna shiga yay parking su sauko ya tasa agaba sunufi office din principal, tunda ga waje yay sallama, principal yace yes ku shigo,

suna shigowa malam sani ya bashi hannu su gaisa, principal yace har yanzu wancen matsalar ce batakare ba? kai malam sani ya girgida yace ba ita bace, wannan wata matsalar ce kuma daban,

principal yace to inajinka meke faruwa? tsaf malam sani ya kwashe labarin da murja ta bashi ya fadawa principal, kai principal ya girgida yace babbar magana, barina aika akira for master dinsu muji koya abin yake,




from the experience of jamilu zazzau

WhatsApp  08104550703
Read More»

Fateema Habeeb 11

Fateema Habeeb   11




                    na
Jamilu el hussain zazzau




           dedicated to
    Amina baba kaduna




washe gari habib na gama shirin school mahaifin shi ya dauke shi a mashin dinsa suka nufi makarantar,

suna shiga harabar school din ya samu waje ya faka mashin din ajikin wata bishiyar dogon yaro dake harabar school din, kai tsaye ya tasa habib agaba sunufi office din principal,

sallama yayi, principal yace bissimilah ku shigo, suna shigowa malam sani ya mika masa hannu su gaisa, sannan ya samu waje ya zauna, habib kuma na gefe yana tsaye,

duk irin halin da habib ke ciki malam sani ya kwashe ya fadawa principal, kadan principal ya dago kai ya kalli malam sani yace gaskiya yanzu ayyuka sun min yawa, saboda haka bazan iya sauraran wannan case din ba, amma yanzu barina hadaka da class master din su domin ya bincika ma,

kallo principal ya watso ma habib, yace jeka staff ka kira min malamin ajinku, da sauri habib yaje staff yakira malam ayuba su dawo tare,

kallon malam ayuba principal yayi, yace malam ayuba wannan bawan Allah da kake gani mahaifin yaron nanne, yazo yay min bayani cewa yaron shi na cikin damuwa matuka, kuma yana tunanin matsalar  daga nan school take, saboda haka abinda nake so dakai katasa keyar yaron nan kuje ka bincike shi yafada maka abinda ke damun sa,

malam ayuba yace ok sir,   kallon habib yayi yace wuce muje, habib na gaba malam ayuba na biye dashi sutafi class din su,

suna shiga students su mike duk su gasshe shi, yace ku zauna, kallon su yayi ya nuna habib yace kunsan wannan? duk su hada baki suce eh, yace ko akwai abinda ya hadashi da wani acikin ku? class kowa ya girgida kai yace aa,

mikewa monitan class din yayi, yace sir gaskiya akwai abinda ke damun shi kwana biyun nan, domin kullum ya shigo class baya kula kowa saide ya koma gefe yay ta tunani, ko walwala beyi da jama'a, kallo malam ayuba ya wurgo ma habib yace mu koma,

agaba ya taso shi su dawo office din principal, kallon su principal yayi yace ma malam ayuba ya akayi? dalla dalla malam ayuba yay mar bayani, principal ya kalli malam sani yace to megida kadai jiko?

malam sani yace eh naji, principal yace to zaka iya komawa idan ya sanar damu zamu nemeka muyima bayani, malam sani yace to madalla nagode, ya basu hannu su gaisa ya fito daga office din, kai tsaye yaje ya dauki mashin din sa yanufi gida,

mahaifin habib na fita principal yakira displine master yace kaga yaron nan akwai abinda ke damun sa, iyayen sa sunyi sunyi dashi yaki fada musu shine su taso keyar shi zuwa makaranta, muma nan mun tambaye shi yaki fada mana, saboda haka abinda nakeso dakai ka tasa shi agaba kuje saiya fada maka,

displine yace ok sir, fuska ya daure ya dakawa habib tsawa yace wuce muje, kai tsaye ya tasa habib zuwa office din shi, suna zuwa yasa habib yasa guiwar sa akasa shi kuma ya jawo kujerarsa ya zauna, sannan ya dauko wata dorina mai baki biyu ya ajiye kusa dashi,

hararan habib yayi, yace to zakai min bayani ko saina zaneka? dago kai habib yayi, yace sir nifa ba abinda ke damuna, barazana displine yay tama habib amma duk da haka baisa habib ya fadi komai ba, ganin haka yace mishi tashi mu koma,

kai tsaye ya taso shi su dawo office din principal, suna dawowa yace ma principal nima nayi nayi dashi yaki fadamin, kallon habib principal yayi, yace tunda kace babu abinda ke damunka tashi ka wuce class, jaka habib ya dauka kai tsaye ya wuce class din su,

zuwa yamma bayan an tashi daga makaranta principal su hadu da mahaifin habib a kasuwa yay mishi bayanin duk yadda su kayi da habib amma yaki fada musu, malam sani yace nagode ba damuwa, sukai sallama ya wuce,




from the experience of jamilu zazzau

WhatsApp  08104550703
Read More»
Follow Admin On Twitter naimismo1
Join Our Newsletter