Saturday, November 30, 2019

Home Fateema Habeeb 16
..
Fateema Habeeb  16



                      na
Jamilu el hussain zazzau



             dedicated to
       Amina baba kaduna




5:00pm habib ya debi ruwa ya shiga wanka, yana fitowa ya shiga daki ya sami versiline dinsa mai kamshi ya shafa, sannan ya sami black trouser da red t shirt ya saka, explorer perfume ya fesa sannan ya sauki takalmi ya saka ya fito, kai tsaye ya nufi gidan su abdurrahaman,

yana zuwa ya iske abdurrahaman zaune a kofar gida yana jiran sa, yace sorry na bata lokaci ko? abdurrahaman yace lallai kam ka kusa makara, murmushi habib yayi yace to musa kai kawai,

tafiya suke suna fira kai tsaye su nufi copper's lodge, a bakin kofa su tsaya su rasa wanda zai shiga yakira musu ita, ana cikin haka sai ga copper yusif ya dawo daga cikin gari, da sauri su taso suzo su gasshe shi, yace wa kuke nema ne? suce copper fatima, yace ok bari nai muku magana da ita, suce thanks sir,

copper yusif na shiga ya iske fatima zaune acikin copper's suna fira, kallon ta yayi yace fati kinyi baki, da sauri ta watso mishi kallo itama, tace baki? murmushi yayi yace students dinki ne, tace oh shine zasu tsaya a waje, copper yusif yace to kila ko kunyar shigowa su keji tashi kije ki shigo dasu,

yunkurawa fatima tayi ta shiga daki ta dauko hijabi ta saka, kai tsaye ta nufi waje, tana fita ta iske su a tsaye, tace oh kune? fuska abdurrahaman ya saki yace wallahi kuwa, bayan sun gaisa tace lafiya ko? kadan abdurrahaman ya sosa kai yace qalau, dama munzo fada miki wani sako ne,

tace ok ina jinku, hannu abdurrahaman yasa cikin aljihun sa ya dauko wannan wasikar daya rubuta ya mika mata, yace ga wannan sakon dake tafe damu yana ciki, 

kallo ta watso mishi tace menene aciki? yace kar ki damu ki bude zaki gani, idan kin karanta habib zaki bama amsa, yana fadin haka ya kalli habib yace abokina minti daya ina zuwa, da sauri ya lallaba yaje jikin wata bishiya ya buya domin yaga abinda zai faru, fatima na budewa taga rubutu kamar haka,

   
         aminci agareki

dafatan kina cikin koshin lafiya kamar yadda nake, a gaskiya fatima tun ranar da Allah yasa nai tozali da kyakkyawar surar ki Allah ya jarabce ni da tsnanin sonki, wannan dalilin yasa nazo domin bayyana miki, ina mai fatan zan sami masauki acikin zuciyar ki, 

        daga masoyinki na har abada habib sani ss3B,

tana gama karantawa ta dago kai ta kalli habib tace waya rubuta wannan wasikar? numfasawa habib yayi yace nine, tun kafin ya rufe baki ta falla mishi mari, tace stupid baka da hankali ne, koka fara shaye shaye ne? idiot ni zaka dubi tsabar idona kace zakai soyayya dani,

da sauri ta koma cikin lodge din ta sanar da sauran copper's abinda ke faruwa, da sauri suka dungumo su fito domin suga wani students ne haka, suna fitowa su iske habib ko motsawa daga wajen da yake tsaye beyi ba,

kallon shi copper yusif yayi yace kai kayi wannan abin? kai habib ya daga yace eh, yusif yace oh dama abinda ya kawo ku kenan? shiru habib yayi yana kallon su kowa na fadan albarkacin bakin sa,

copper yusif yace baku da hankali, amma zakuyi nadamar abinda ku aikata, kusa da habib copper kadija ta matso takira copper yusif tace kunga ku mishi hakuri yanzu, idan ya sake saiku dau mataki,

kai copper yusif ya girgida yace no, bawani hakurin da zatayi dolene ya fuskanci hukunci domin nan gaba ya zame mishi darasi,

can gefe copper kadija taja habib tace mishi meyasa kai haka? hawaye ne suka fara zuba daga idanuwan sa yafara magana cikin rawar murya,




Domin samin littafin daga na daya zuwa inda mu tsaya saika tuntubeni ta wannan number dake kasa,



from the experience of jamilu zazzau

WhatsApp  08104550703
No comments:
Write comments

Follow Admin On Twitter naimismo1
Join Our Newsletter