Saturday, November 30, 2019

Home Fateema Habeeb 17
..
Fateema Habeeb  17



                     na
Jamilu el hussain zazzau



     
             dedicated to
       Amina baba kaduna




malama nima banyi kaina bane, domin tun ranar dana ganta zuciya ta ta kamu da sonta, tun a wancan lokacin nai kokarin kawar da soyayyar da karfi amma abin yafi karfi na, domin a sanadiyar afkawa soyayyar ta har matsala na samu da iyayena, baya ga nan na samu matsala da malamai na, na kuma amshi horo da azabtarwa iri daban daban,

saboda haka tunda na riga na furta na gummace na mutu akan na janye abinda ke zuciya ta, tace oh yanzu habib kana nufin bazama ka janye wannan maganar bama kenan? yace wallahi malama bazan iya ba, idan na janye mutuwa zanyi, saboda haka na dauki damarar jure duk wata wahala da zata biyo bayan yin hakan,

jin wadan nan jerin kalaman daga bakin habib yasa jikin copper kadija yay sanyi, tashi guda tausayin shi ya kamata, tace kabari zan sameta a tsanake na fahimtar da ita duk yadda muyi zan sanar dakai, yace nagode saida safe, tace Allah ya kaimu,  kai tsaye habib ya kama hanyar gida, ita kuma ta koma cikin lodge din,

copper kadija na shiga kai tsaye taje daki ta iske fatima, kusa da ita ta samu waje ta zauna agefen katifa, tace kawa inason muyi magana akan habib, fatima tace umhum ina jinki, kallo kadija ta watso mata tace a zahirin gaskiya bazan boye miki ba yaron nan ya kamu  tsananin soyayyar ki, game da labarin irin halin daya shiga akan soyayyar ki yasa jikina yayi sanyi sosai, tabbas na tausaya mishi,

kallo fatima ta jefo mata, tace yanzu me kike nufi? numfasawa kadija tayi tace ki taimaka ki ceto rayuwar shi, yatsine fuska fatima tayi tace me kike nufi dana ceto rayuwar shi? kadija tace ina nufin ki amshi soyayyar shi,

rai abace fatima tai girgida kai tace kin raina min hankali, in banda kin raina min wayau ni zaki kalla kice nai soyayya da students dina, wanda na tsere mishi ta kowani fanni,

numfashi kadija taja, sannan ta girgida kai tace wannan ba rainin wayau bane kawai zan iya cewa wani al amari ne daga ubangiji, domin shi Allah yana iya sarrafa al amarin sa takowani fanni kuma a lokacin da yaga dama, idan zaki tuna tarihin mazon Allah (s a w) lokacin da uwar muminai nana kadija ta aure shi aita girme shi sannan ta fishi arziki, saboda haka a tunanina ma yin hakan koyi da sunna ne,

buder bakin fatima tace ai naga kema mace ce, idan da gaske ki keyi kin tausaya mishi kamata yayi ki amince ki aure shi, kai kadija ta dago ta kalle ta, tace kar ki manta tare ya ganmu amma ya zaba cewa ke yake so,

cikin fushi fatima tace to bana son shi, ko ana so dolene? kuma na rantse miki saina sa an hukunta shi, domin ya zame mishi darasi nan gaba, kadija tace ba damuwa Allah ya taimaka, tana fadin haka ta tashi ta fita,

washe gari da sassafe abdurrahaman ya dauki waya yakira habib, habib na dubawa ya daga gami da girgida kai, abdurrahaman yace hello abokina ya akayi ne? numfashi habib yaja yace normal, abdurrahaman yace wai jiyan nan ya kuka kare dasu ne? habib yace abinda kasani miye kuma na tambaya,

murmushi abdurrahaman yayi, yace malam habib kenan yanzu menene mafita? numfashi habib yaja, yace yadda Allah yay damu haka za ayi,

dariya abdurrahaman yayi, yace gaskiya abokina ina baka shawara kada kaje school yau, domin komai na iya faruwa, numfashi habib yaja, yace zanje domin na tabbatar ba kashe ni za suyi ba, abdurrahaman yace babu maganar kisa amma zasu kashe ma fatar jiki,

tsaki habib yaja ya kashe wayar shi ya koma ya cigaba da baccin sa, gari na gama wayewa ya tashi ya shiga wanka, yana fitowa ya shafa mai ya saka uniform, yana gama break fast ya dauki jaka yanufi school,




me karatu ya kake gani zata kaya, domin sanin hakan sai kayi kokari ka nemi cigaban labarin




from the experience of jamilu zazzau

WhatsApp  08104550703
No comments:
Write comments

Follow Admin On Twitter naimismo1
Join Our Newsletter