Friday, November 29, 2019

Home Fateema Habeeb 15
..
Fateema Habeeb  15



                     na
Jamilu el hussain zazzau


       dedicated to
   Amina baba kaduna



Habeeb na karisawa jikin katuwar bishiyar nan ya hau ya sauko da jakar sa dake gurin, daya bayan daya ya fara kallon hotunan fatima, yana gamawa ya mayar ya aje, duk abinda ya keyi abdurrahaman na makale ajikin wata bishiya yana kallon shi,

habib na mayar da jakar ya kama hanya ya nufi cikin school, ganin yayi nisa abdurrahaman ya fito daga wajen da yake, kai tsaye yaje ya hau bishiyar ya sauko da jakan,

bude wa yayi domin yaga abinda suke ciki, yana budewa yaga pictures din copper fatima ne aciki masu kyau tare da kalaman soyayya, kallon su yafara yi daya bayan daya, a bangaren habib kuwa harya kusa shiga cikin school zuciyar shi ta bashi cewa ya koma wajen jakar nan, kawai ya biye mata kai tsaye ya juyo,

tun daga nesa ya hangi abdurrahaman rike da hotunan nan yana kallo, harya iso wajen abdurrahaman baisan ya dawo ba, kadan habib yaja numfashi yace sannu da aiki,

a tsorace abdurrahaman ya zubar da hotunan ya waigo, yana waigowa yaga ashe habib ne ya dawo, yace oh dama baka wuce ba? habib yace ok dama jira kake na wuce kenan?

kai abdurrahaman ya girgida yace aa, habib yace tome ya kawo ka nan? abdurrahaman yace dama zuwa nayi naga wajen da kake zuwa kana hutawa,

murmushi Habeeb yayi, yace yaro nasan meya kawo ka saboda haka barina ja maka kunni, kada ka sake kaba wani wannan labarin, karfin hali abdurrahaman yayi yace haba ai baka isa ba wallahi, domin ina tashi daga nan gidanku zanje na fadawa maman ka, kaga yanzu shikenan zata san abinda ke damun ka,

cikin bacin rai habib ya kalle shi yace haka kace ko? tabbas saina fada musu, domin babu abinda zai hanani fada, kai habib ya girgida yace jikinka ko zai fada maka,

tsimagiya ya dauko ya tunkaro abdurrahaman da ita, ganin haka yasa abdurrahaman yay dariya yace matsala ta dakai bakasan wasa ba wallahi, jin haka yasa habib ya yar da tsimagiyar ya samu waje ya zauna,

kallon abdurrahaman yayi yace abokina tunda Allah yasa yanzu kasan abinda ke faruwa menene shawara? murmushi abdurrahaman yayi yace shawarar kenan kawai ka fito fili ka fada mata cewa kana sonta koma menene zai faru ya faru,

kai habib ya girgida yace wannan ba shawara bace, ko so kake akara azabtar dani? abdurrahaman yace bazata bari akara azabtar dakai ba muddin ta amince, habib yace to naji, idan kuma bata amince bafa?

kai abdurrahaman ya dago yace kar ka damu ni nasan yadda za ayi ta amince, habib yace ok, toya zamuyi mu tunkare ta?

abdurrahaman yace kaga kabar komai agurina zuwa nan da gobe, murmushi habib yayi yace kai amma gaskiya nayi matukar farinciki da zuwan ka,

tattara hotunan habib yayi ya mayar acikin jakar ya hau bishiyar ya sagale sannan ya sauko su kama hanya su koma cikin makaranta,

washe gari suna zaune a cikin class habib ya kalle shi yace ya maganar mu? abdurrahaman yace ban manta ba ai, amma ba'a school zamu fada mata ba kabari sai an tashi sai muje har copper lodged din mu sameta, habib yace ok Allah ya kaimu,

jim kadan abdurrahaman ya yagi wani fallen paper ya rubuta duk wasu bayanai dasu dace su fada mata, yana gamawa ya ninke ya saka a aljihu,

ana tashi school yace ma habib zuwa yamma idan ka shirya saika biyo ta gidanmu mu wuce, Habeeb yace ok ba damuwa sai anjiman,



Hammm me karatu shin ya kake gani, zata iya amince wa kuwa? domin tabbatar da hakan sai kuyi dakon cigaba,



from the experience of jamilu zazzau

WhatsApp  08104550703
No comments:
Write comments

Follow Admin On Twitter naimismo1
Join Our Newsletter