Friday, November 29, 2019

Home Fateema Habeeb 14
..
Fateema Habeeb  14



                     na
Jamilu el hussain zazzau



             dedicated to
        Amina baba kaduna




Washe gari da sassafe habib ya shiga wanka, yana fitowa yay shirin school, sannan ya fito ya karya, jaka ya dauka zai fita malam sani ya harare shi yace idan kaso kar kaje school din ka wuce wani wajen,

kai tsaye habib ya kama hanya sai school, yana isa ya zame class,

displine na zuwa ya wuce wajen aikin da yasa habib domin ya duba ya gani ko yayi, yana zuwa ya iske habib ya gama aikin tsaf, girgida kai displine yayi yace lallai yaron nan yakai tantiri ace mutum ya gummace yay ta shan duka sai kace jaki, kai tsaye ya wuce office din principal yay mishi bayani cewa sir babu inda banyi da yaron nan ba, amma yaki fadamin wajen da yake zuwa,

principal yace kar ka damu jeka abinka ni nasan yanda zanyi dashi, domin naci uban wanda suka fishi gagara, ana tashi break principal yaje har class din su habib ya taso shi agaba zuwa office din sa,

kallo ya watso mishi yace sa guiwar ka akasa, da sauri habib yasa, yace inason kai min bayanin wajen da kake zuwa baka son zuwa school, domin kaga wannan yawon da kakeyi kanka kake zalunta,

shiru habib yayi yaki magana, tsawa principal ya daka mishi yace ba dakai nake magana ba? yace sir ba inda nake zuwa, murmushi principal yayi yace wato har yanzu baka daku ba kenan tunda kaki bayani,

rai abace principal ya kalle shi yace tashi ka kama kunninka awajen, ba gardama habib ya tashi ya kama, principal yay ta aikin shi har ya manta dashi, zuwa can hawaye suyi ta zubo masa kafafuwan sa sukai tsami ya yanke jiki ya fadi,

jin karar faduwar sa yasa principal ya dago dakai ya kalle shi yace ubanwa ya tashe ka? bulala ya dauko yafara tsula mishi, yana fadin dan ubanaka fadamin ina kake zuwa bakasan zuwa school, ihu kawai habib keyi yana fadin kayi hakuri malam babu gurin da nake zuwa,

jin haka yasa principal yace stupid kawai, tashi ka wuce class, da kyar habib ke tafiya, kai tsaye ya koma class,

bai jima da fita daga office din principal ba sai ga mahaifin sa yazo, bayan sun gaisa principal yay ma malam sani bayanin duk irin punishment din da suyi ma habib amma yaki fada musu wajen da yake zuwa, malam sani yace to ba damuwa ku kyale shi nagode, hannu ya bashi sukai sallama ya kama hanya ya koma,


5:pm malam sani ya dawo daga kasuwa, dai dai lokacin habib na zaune a tsakar gida rike da wani karamin littafi yana karatu, kallo ya watso mishi yace wato kaki musu bayani ko? na sake jin ance baka zuwa kagani nida kaina zan casa ka, shiru habib yayi baice komai ba,

washe gari Habeeb na gama shirya wa zai fita murja tace to habib dan Allah ka mayar da hankali kaji, yace to, tace a dawo lafiya, yana fita kai tsaye ya wuce school,

yana shiga class ya ajiye jakarsa ya fito, kai tsaye yanufi bayan gari wajen daya ajiye hotunan fatima, tun daga nesa abokin shi abdurrahaman ya hange shi, da sauri ya kama hanya ya bishi abaya,

zuwa can habib yaji kamar ana biye dashi, da sauri ya waigo  ya duba, abdurrahaman kuma yay sauri ya boye a jikin bishiya, ganin baiga kowa ba yasa ya cigaba da tafiya, abdurrahaman ya fito ya cigaba da binsa,



from the experience of jamilu zazzau

WhatsApp  08104550703
No comments:
Write comments

Follow Admin On Twitter naimismo1
Join Our Newsletter