Fateema Habeeb 01
na
Jamilu el hussain zazzau
dedicated to
Amina baba kaduna
Bissimillahirrahamanirrahim
Misalin yamma lokacin rana ta fada, ga iska mai dadi na kadawa tako ina, masoyan ke zaune acikin farfajiyar gida suna fira,
cikin sassanyar murya gami da lumshe ido fatima ta kalli kamal, tace hubby ji nake kamar na fasa zuwa wannan bautar kasar, kadan kamal yay murmushi tare da cewa fatima kenan nima tuntuni nake zullumin zuwan wannan lokacin, domin rabuwar mu abune mai taba zuciya, gashi garin da zakuje gurine mai nisa balle na rika kawo miki ziyara lokaci bayan lokaci, tabbas zan zama abin tausayi muddin idanuwa na suka daina tozali da wannan kyakkyawar surar taki,
kadan fatima tai ajiyar zuciya tace hubby kana jefani cikin kogin tunani mai tsananin zurfi aduk lokacin daka tasani agaba da irin wadan nan tausasan kalaman naka masu ratsa, zuciya, dolene nai bakin ciki da juyayin rabuwa dakai,
murmushi sahibin yayi, yace kar ki damu, na miki alkawarin bazaki taba missin din muryata ba, domin tana tare dake akoda yaushe, kuma ina miki albishir cewa ko ina kije muryata tana biye dake ta waya domin isar da sakonnin soyayya agareki,
babu abinda zai zama cikas agaremu illa rashin ganin fuskokin juna, kadan ya saki numfashi, yace koda yake muna da picture din juna, duk da nasan cewa photo bazai iya gamsar da zuciya ababen da take bukata ba, amma zai rage mata zafin radadin da take ji,
dogon numfashi fatima taja, gami da jefo mishi wani munafukin kallo tace hakane hubby, photo bazai iya gamsar damu ba kamar ace gamu tare, amma zai kasance mana garkuwa da kuma ragema zuciya radadin halinda zata tsinci kanta,
kadan ta sake numfasawa tace, duk da nasan cewa zuciya ta karama ce aduk lokacin data sami matsala akan soyayyar ka zata iya fashewa, da sauri kamal ya katseta, yace ki daina irin wannan tunanin, dolene mubaiwa zukatan mu hakuri, tunda a tsari wannan tafiya taku ta zama dole, cikin kan kanin lokaci idanun fatima su kada kamar hawaye zasu zubo mata, kallon ta kamal yayi, yace kinga banason ganin hawayen ki awaje domin hakan na taba min zuciya, ki kwantar da hankalin ki tafiya ba mutuwa bace, shiru tayi tana sauran shi, sannan ya dago kai ya kalle ta yace zanzo na wuce, sai munyi waya, tace ok muje na taka ma, atare su jera har jikin motar sa suna tafiya suna fira, ya bude mota ya shiga, saida ya wuce sannan ta nufi cikin gida,
hajia ce zaune bisa kujera fatima tai sallama ta shigo, kadan hajia ta dago da kanta ta amsa, cikin sakin fuska fatima tace momy nusaiba basu dawo bako? hajia tace eh, basu shigo ba tukun, cikin daki fatima ta shige ta cire hijabi ta dawo falo ta zauna,
sautin sallama suji, nusaiba ce tare da bashir su dawo daga islamiyya, da sauri bashir yaje ya rungumi hajia, murmushi hajia tayi gami da dafa kansa, tace baby boy an dawo? bashir yay dariya yace eh mom, tace ok jeka aje bag din ka cire uniform ko, yace to, waje nusaiba ta samu ta zauna,
jim kadan hajia taji sautin kiran sallah, kallo ta watso musu, tace to kutashi kuje kuyi sallah, atare nusaiba da fatima su tashi zuwa cikin daki, kowa taje tai alwala tai sallah,
8:00pm duk su dawo dinning suna cin abinci suna fira, hajia ta kalli fatima tace kamar naji ance gobe ana nemanku a school ko? kai fatima ta daga tace eh, karfe tara suce muzo, hajia tace ok Allah ya kaimu, fatima tace amin,
from the experience of jamilu zazzau
WhatsApp 08104550703










No comments:
Write comments