Wednesday, November 27, 2019

Home Fateema Habeeb 05
..
Fateema Habeeb  05



                     na
Jamilu el hussain zazzau




           dedicated to
   Amina baba kaduna




4:00pm suka isa garin saminaka,
saminaka babban garine, dake da attajirai da yan kasuwa da kuma manyan manoma,

Government secondary school dake garin atura su fatima, suna shiga garin sukai tambaya direct a nuna musu gurin da makarantar take,

suna isa school din su iske bakowa an riga an tashi, sai wani class guda daya dake da mutane aciki suma meeting din addini ya dawo dasu,

waje suka samu sukai parking su sassako,
ganin su yasa wani teacher daga cikin masu meeting din nan ya taso yazo,

bayan sun gaisa sukai mishi bayanin komai game dasu, waya ya dauka yakira principal ya fada mishi, principal yace ok jeka ka kaisu masauki,

teacher din yace to muje ko, yay gaba suka bishi abaya zuwa copper's lodge, suna isa suka iske masu bautar kasa da yawa wadan da aka turo daga wasu states din,

hostel din da zasu  zauna ya nuna musu, sannan yasa a kawo musu abinci,

jim kadan da gama cin abincin su fatima ta dauki waya takira kamal, dai dai lokacin sahibin na kwance bisa katuwar katifar sa yana tunanin ta,

da sauri yasa hannu ya dauko wayar, gami da tausasa murya ya kara a kunni, hello sahiba, murmushi tayi cikin sassanyar murya tace na'am hubby yakake? qalau nake har kun sauka kenan?

eh wallahi yanzu ma haka muna cikin masaukin mu, ajiyar zuciya yayi, yace tanx god toya gajiyar hanya? kadan tai murmushi tace gaskiya garin akwai nisa mungaji sosai,

yace oh Allah sarki, to yanzu abinda ya dace kije ki watsa ruwan sanyi sannan ki kwanta ki huta ko, tace umhum sai anjima, yace ok bye, cike da jindadi ta sauke wayar sannan ta lalubo number mom dinta ta kira,

dai dai lokacin hajia na zaune a falo nusaiba na mata tausa, fuska cike da annuri hajia ta daga wayar, hello maman baban ta har kun isa kenan? murmushi fatima tayi tace eh mom, hajia tace ok toya hanya? tace lafiya qalau mom, hajia tace yayi kyau toya ya nayin garin?

kadan ta numfasa tace ba laifi garin yana da dan girma ba kauye bane sosai, hajia tace ok yayi kyau, sannan ta mikawa nusaiba wayar su gaisa,

suna gama wayar ta yunkura ta dauko bokiti ta debi ruwa ta shiga bandaki ta watsa, tana fitowa ta gyara katifa ta kwanta, kadija na zaune kusa da ita suna fira har bacci ya kwashe ta, ganin bacci ya kwashe fatima yasa kadija ta fito waje gurin sauran copper's su cigaba da fira,

zuwa faduwar rana fatima ta farka, tana farkawa ta sake diban ruwa ta shiga toilet tai wanka, tana fitowa ta bude jakarta ta dauko lotion mai kamshi ta shafa,

sannan ta dauki dogon siket ta saka gami da wata karamar t shirt mara nauyi, wani karamin mayafi ta yafa ta fito, dai dai lokacin itama kadija ta gama shiryawa, kai tsaye su fita cikin gari,




from the experience of jamilu zazzau

WhatsApp    08104550703
No comments:
Write comments

Follow Admin On Twitter naimismo1
Join Our Newsletter